Hisbah ta yi barazanar gurfanar da masu tashe a kotu
Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta yi barazanar kai duk wanda aka kama yana gudanar da tashe zuwa kotu, sakamakon yadda wasu ke amfani da al’adar wajen aikata laifuka da tayar da hankalin jama’a.
A wata sanarwa da Mataimakin Babban Kwamandan hukumar, Dakta Mujahiddin Aminuddin, ya fitar, ya ce wasu bata-gari na amfani da tashe wajen yin sare-sare, doke-doke da cin mutuncin mutane, a wasu lokuta har da firgita al’umma.
Ya tunatar da jama’a cewa watan Ramadan lokaci ne na ibada, istigfari, tuba, rahama da kuma ‘yantar da bayi daga wuta. Ya kara da cewa bai dace a rika amfani da sunan Musulunci ko addini wajen cin mutunci ko cin zarafin wani ba, domin hakan ya sabawa koyarwar addini.
Dakta Aminuddin ya yi kira ga al’umma da su bi doka tare da guje wa duk wani abu da zai iya kawo hargitsi. Ya kuma gargadi cewa duk wanda hukumar ta kama da hannu a irin wadannan ayyuka, za a gurfanar da shi a kotu domin ya fuskanci hukunci daidai da laifin da ya aikata.
Comments
Post a Comment