Posts

Showing posts from February, 2026

Iran ta kai harin ramuwar gayya kan Israel da Amurka

Image
An ji karar fashe-fashe a yankin Haifa da ke arewacin Isra’ila a ranar Asabar bayan harba makamai daga Iran, kamar yadda kafar yada labarai ta Isra’ila Ynet ta rawaito. Tun da fari, kararrawar gargadin hare-haren sama ta yi kara a sassa daban-daban na Isra’ila bayan da sojojin kasar suka sanar da gano makamai masu linzami da aka harba daga Iran zuwa cikin kasar. A safiyar Asabar ne Isra’ila ta kaddamar da wani hari kan Iran mai taken “Lion’s Roar”, inda ta ayyana dokar ta-ɓaci ta musamman da gaggawa a fadin kasar. A nasa bangaren, Shugaban Amurka, Donald Trump, ya tabbatar da cewa ana gudanar da “manyan ayyukan yaki” a Iran, yana mai cewa manufar hakan ita ce kare al’ummar Amurka ta hanyar “kawar da barazanar da ke tafe daga gwamnatin Iran.” Gidan talabijin na kasar Iran ya kuma rawaito cewa sojojin Iran na kai hare-hare kan sansanonin sojojin Amurka da ke yankin.

Jam’iyyun siyasa na fuskantar yiwuwar hana su shiga zaɓen 2027 kan rajistar mambobi ta yanar gizo

Image
Jam’iyyun siyasa na iya rasa damar tsayar da ’yan takara a zaɓen 2027 idan ba su bi sashe na 77 na dokar zaɓe ta 2026 ba kamar yadda jaridar TheCable ta rawaito. A ranar 18 ga Fabrairu, Shugaba Bola Tinubu ya rattaba hannu kan dokar gyaran zaɓe bayan majalisar tarayya ta amince da ita. Sashen na 77(2) ya tanadi cewa dole jam’iyyun siyasa su miƙa cikakkiyar rajistar mambobinsu ta yanar gizo ga INEC aƙalla kwanaki 21 kafin gudanar da zaɓen fidda gwani. Rajistar dole ta ƙunshi sunaye, jinsi, ranar haihuwa, adireshi, jiha, ƙaramar hukuma, gunduma, rumfar zaɓe, lambar shaidar ɗan ƙasa (NIN) da hoto, a takarda da kuma a na’ura. Sashen na 77(7) ya ce duk jam’iyyar da ta gaza miƙa rajistar cikin wa’adin da aka kayyade ba za ta samu damar tsayar da ɗan takara ba. INEC ta fitar da sabon jadawalin zaɓe, inda ta sanya 16 ga Janairu, 2027, a matsayin ranar zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar tarayya, sai 6 ga Fabrairu, 2027, don zaɓen gwamnoni da majalisun jihohi. Ta kuma umarci jam’iy...

John Oyegun: Shugabannin ADC na Kudu maso Kudu sun amince da takarar Amaechi a 2027

Image
John Odigie-Oyegun, tsohon gwamnan Edo, ya ce shugabannin ADC na yankin Kudu maso Kudu sun amince da kudirin takarar shugaban kasa na Rotimi Amaechi, tsohon ministan sufuri kamar yadda jaridar TheCable ta rawaito. Oyegun ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin taron tuntuba na shugabannin ADC na Kudu maso Kudu da aka gudanar a Benin City, babban birnin jihar Edo. Ya ce Amaechi ya sanar da shugabannin yankin Kudu maso Kudu aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa. “Mun yi farin ciki cewa ɗanmu, Rotimi Amaechi, ya yi amfani da wannan taro wajen sanar da mu a hukumance aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa ta wannan babbar ƙasa tamu,” in ji Odigie-Oyegun. “Zan iya sanar da ku cewa an cimma matsaya baki ɗaya domin ba shi dukkan goyon bayan da yake buƙata wajen cimma burinsa.” A watan Yuli na shekarar 2025, Amaechi ya ce zai amince ya yi wa’adi guda ɗaya kacal idan ya samu tikitin takarar ADC kuma ya lashe zaɓen shugaban kasa na 2027. A farkon wannan wata, tsohon ministan ...
NBTE Ta Amince da Sabbin Kwasa-kwasan Karatu 18 ga Nuhu Bamalli Polytechnic, Zaria

Rector Drives Institutional Growth as NBTE Grants Fresh Programme Approvals to Nuhu Bamalli Polytechnic

Image
The National Board for Technical Education (NBTE) has granted approval to Nuhu Bamalli Polytechnic, Zaria, Kaduna State, to commence 18 additional academic programmes beginning from the 2025/2026 academic session. This was contained in an official letter dated February 20, 2026, signed by the Director of Polytechnic and Allied Programmes Department, Dr. Mrs. Fatima Kabir Umar, on behalf of the Executive Secretary of NBTE, Prof. Idris M. Bugaje, following a Digital Resources Inspection Verification exercise conducted at the institution between January 27 and 28, 2026. According to the Board, the newly approved programmes cut across engineering, science laboratory technology, agriculture, media studies, law and management disciplines. Among the programmes approved are HND Agricultural and Bio-Environmental Engineering, HND Computer Engineering Technology, ND Mechatronics Engineering Technology, ND Renewable Energy Technology, HND Journalism and Media Studies, HND Film and Mul...

EFCC ta sake gurfanar da Malami, matarsa da ɗansa kan zargin “badakalar kuɗi”

Image
Hukumar yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta EFCC ta sake gurfanar da tsohon Antoni Janar na ƙasa (AGF), Abubakar Malami, tare da matarsa, Asabe Bashir, da ɗansa, Abdulaziz, bisa zargin aikata laifin badakalar kuɗi. An sake gurfanar da waɗanda ake tuhuma a ranar Juma’a a gaban Joyce Abdulmalik, alkaliyar babbar kotun tarayya da ke Abuja, bayan da aka sauya alƙalin da ke sauraron shari’ar. A zaman da aka koma ci gaba da shari’ar, lauyan hukumar EFCC, Jibrin Okutepa, ya shaida wa kotu cewa shari’ar na zuwa ne karo na farko a gaban sabuwar alkaliyar da aka ba ta, sannan ya roƙi kotu da ta karɓi amsar tuhumar daga bakin waɗanda ake zargi.

Ficewar Fintiri daga PDP zuwa APC, illace babba ga Atiku a jihar Adamawa

Image
Mai bai wa Shugaba Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai Bayo Onanuga, ya bayyana sauyin sheƙar Gwamnan Adamawa, Ahmadu Fintiri, zuwa jam’iyyar APC a matsayin babban sauyi na siyasa da zai bai wa jam’iyyar rinjaye a jihar. A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Juma’a, Onanuga ya ce matakin da Fintiri ya ɗauka na ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa APC zai ƙara wa jam’iyyar da ke mulki ƙarfi a Adamawa, yana mai cewa wannan lamari babbar illa ce ga Atiku Abubakar. Ya bayyana cewa sauyin ya shafi makomar siyasar jihar gaba ɗaya, musamman yayin da zaɓen shugaban ƙasa ke ƙaratowa.

INEC ta mayar da lokacin zaɓen 2027 kafin Azumi

Image
Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC ta sanya ranar 16 ga Janairu, 2027, a matsayin sabuwar ranar gudanar da zaɓen Shugaban Ƙasa da na ‘yan Majalisar Tarayya. Haka kuma, hukumar ta ayyana ranar 6 ga Fabrairu, 2027, a matsayin sabuwar ranar gudanar da zaɓen gwamnonin jihohi da na ‘yan Majalisun Dokokin Jihohi. A sanarwar da hukumar ta fitar ta bayyana cewa za a gudanar da zaɓen fidda gwani na jam'iyyun daga watan Afrilu zuwa Mayu na 2026

DSS ta saki Walida wacce ake zargin an sace ta, an sauya mata addini a Jigawa

Image
Hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta saki Walida Abdulhadi Ibrahim, yarinyar da aka sace daga jihar Jigawa , tare da miƙa ta ga Gwamna Umar Namadi a hedikwatar hukumar da ke Abuja. Gwamnan ya ce za a ci gaba da riƙe Walida a kulawar gwamnatin jihar har sai kotu ta warware dukkan muhawarar da ke tattare da zargin sace ta, sauya addini da kuma batun kulawa da ita. Ya tabbatar da cewa za a ba ta cikakken tsaro tare da kula da lafiyarta, inda ya ƙara da cewa jaririyar da ta haifa ma za ta kasance a kulawar gwamnati. Babban Daraktan DSS, Adeola Oluwatosin Ajayi, ya ce tsare ta da aka yi tun Janairu ya kasance ne domin bin doka da kuma kare lafiyarta yayin da ake bincike.  Ya ce duk da miƙa ta ga gwamnatin Jigawa, DSS da sauran hukumomi za su ci gaba da sa ido kan lamarin. An dai sace Walida ne tun 2023 daga Hadejia, sannan daga baya ta tsinci kanta a Abuja tare da wani jami’in DSS mai suna Ifeanyi Onyewuenyi, wanda ke ci gaba da tsare a hannun hukumar domin bincike.

Ƴan majalisar Adamawa 15 da kakakin majalisa sun fice daga PDP gabanin sauyin sheƙar Fintiri

Image
Wasu ƴan majalisar dokokin jihar Adamawa guda 15 sun yi murabus daga jam’iyyar PDP. Kakakin majalisar, Bathiya Wesley, ne ya sanar da ficewar ‘yan majalisar a zaman majalisa na ranar Laraba. Wesley ya ce shi ma tare da mataimakinsa, Buba Jijiwa, sun fice daga jam’iyyar mai mulki a jihar. Ƴan majalisar sun danganta ficewar tasu da “rikicin da ya daɗe yana ci gaba” a cikin PDP. “Dukkan wasiƙun da aka karanta suna ɗauke da saƙo iri ɗaya. Mambobin PDP sun nuna rikicin da ke faruwa a matakin ƙasa na jam’iyyar a matsayin babban dalilin da ya sa suka yanke shawarar ficewa,” in ji Wesley. “Sun kuma yaba wa PDP bisa ba su damar tsayawa takara da kuma cin zaɓe a ƙarƙashin tutar jam’iyyar.” Daga cikin ‘yan majalisar da suka fice akwai Kefas Calvin, Bulus Geoffrey, Haruna Jilantikiri, Kefas Emmanuel, Ahmed Belel, Moses Zah, Kate Mamuno, Pwamwakeno Mackondo, Adun Alaba, Bulus Kantom, Musa Kallamu, da Japhet Hammanjabu. Jaridar TheCable ta rawaito cewa ‘yan majalisar sun koma jam’iyyar A...

DSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a Edo

Image
Jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS sun kama mutum na shida da ake zargi da hannu a kitsa harin da aka kai a cocin Katolik na St. Francis da ke Owo a jihar Edo a shekarar 2022, wanda ya yi sanadiyar mutuwar fiye da masu ibada 40 tare da jikkata wasu da dama. Tun da farko, hukumar ta riga ta kama mutum 5, inda suke fuskantar shari'ar aikata laifukan ta’addanci, yayin da mutum na shida da aka kama na baya-bayan nan, mai suna Sani Yusuf, ya shafe kusan shekara huɗu yana ɓuya kafin a kama shi a wata unguwa mai suna Iguosa da ke ƙaramar hukumar Ovia North Local Government Area a jihar Edo. Wata majiyar tsaro ta bayyana cewa Yusuf wani babban kwamanda ne a ƙungiyar ISWAP kuma bayan harin Owo ya tsere zuwa Kano kafin daga bisani ya koma ɓuya a yankin na Edo. Rahotanni sun ce ya amsa laifin yana da hannu a harin da aka kai cocin da kuma wasu hare-haren ƙungiyar, ciki har da farmakin da aka kai a barikin sojoji na Suleja a watan Yulin 2022 da kuma sace-sacen mutane a Kaduna ...

Gwamnatin jihar Legas ta kama mutane 46 saboda yin bahaya a fili

Image
Gwamnatin Jihar Legas ta ƙara ƙarfafa hukunta masu yin bahaya a fili, inda ta kama mutane 46 a sabon aikin sintiri da aka gudanarwa a manyan titunan kasuwanci na Tsibirin Legas. Hukumar ta aiwatar da kamun ne ta hanyar rundunar yaƙi da yin bayan gida a Fili ta Jihar Legas a safiyar wannan makon, inda aka mayar da hankali kan wuraren da aka gano rashin tsaftar muhalli, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin da ake yi na aiwatar da dokokin muhalli da kare lafiyar jama’a. Daraktan gudanarwa kuma shugaban hukumar Kula da shara ta Legas, Dr. Muyiwa Gbadegesin, ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin hukuma na gwamnatin jihar a ranar Talata. Sanarwar ta ce, “Gwamnatin Jihar Legas, ta hanyar Rundunar Yaki da Yin Bayan Gida a Fili, ta kama maza da mata 46 masu laifi a yayin wani aikin sintiri da aka tsara da aka gudanar a safiyar yau a fadin Tsibirin Legas.”