Rundunar tsaro ta Civil Defence za ta tura dakaru 11,000 da za su ba da kariya ga manoma a Daminar 2026
Mai magana da yawun hukumar, Babawale Afolabi, ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da jaridar Sunday Punch, inda ya ce hukumar na daukar matakai masu karfi domin tabbatar da tsaron manoma da kuma kare harkokin noma a kasar.
A cewarsa, shugaban hukumar NSCDC, Abubakar Audi, ya sake jaddada kudurin hukumar na tura jami’an da aka horar musamman zuwa wuraren noma domin kare rayukan manoma da dukiyar da ta shafi noma.
Matakin na zuwa ne bayan jerin hare-hare da suka faru kan manoma a wasu sassan Najeriya a shekarar 2025.
Comments
Post a Comment