Sojojin Najeriya sun kuɓutar da mutum 19 da aka sace a Abuja


Jami'an tsaron Najeriya sun ce sun kuɓutar da mutum 19 da aka yi garkuwa da su a Abuja, babban birnin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da sojojin ƙasar suka fitar ranar Asabar, sun ce sun kubutar da mutanen a lokacin wani samamen hadin gwiwar jami'an tsaron ƙasar a ƙauyen Gidan Dogo da ke yankin ƙaramar hukumar Bwari.

Sanarwar ta ce jami'an suin kai samamen ne bayan samun bayanan sirri kan maɓoyar ƴanbindigar da suka sace mutanen.

Sojojin sun ce an kashe mutum ɗaya cikin wadanda ake zargi da satar mutanen, yayin da sauran suka gudu, wasu da raunuka.

Satar mutanen domin neman kudin fansa na ci gaba da yawaita a ƴan shekarun nan a Najeriya, inda ƴanbindigar ke far wa garuruwa da tare kan manyan tituna domin satar mutane.

Duk da cewa a baya matsalar ta fi yawa yankin arewa maso yammcin ƙasar, a baya-bayan nan ta yi naso zuwa Abuja, babban birnin ƙasar.

Comments

Popular posts from this blog

Zazzau Emir’s Defamation Case: Court Bars Claimant Over Non-Compliance, Adjourns Proceedings

Alleged 419 Case: Senator Abdu Kwari in Fresh Court Battle Over Property Deal

Maradin, Dan Saran and Wakilin Watsa Labaran Zazzau Honour Loyal Aides with Traditional Titles