Kotu ta yanke wa wani mutum ɗaurin rai-da-rai bisa yi wa ƴar shekara 9 fyaɗe a Jigawa



Kotu ta yanke wa wani mutum mai suna Bashir A. Umar hukuncin ɗaurin rai-da-rai bayan an kama shi da laifin yi wa yarinya ƴar shekara 9 fyaɗe har ya raunata ta a Jihar Jigawa.

Tun a bara kotu ta samu Umar da laifin, sannan ta yanke masa hukuncin daurin rai-da-rai kan laifin fyade, da kuma ɗaurin shekaru 7 kan laifin jikkata yarinyar.

Haka kuma, kotun ta umarce shi ya biya diyyar naira miliyan 1 ga yarinyar.

Gwamnatin jihar ta yaba da hukuncin, tana cewa adalci ya tabbata. 

Gwamnatin ta kuma kula da lafiyar yarinyar tare da taimaka wa iyayen ta da kyautar gida.

Comments

Popular posts from this blog

Zazzau Emir’s Defamation Case: Court Bars Claimant Over Non-Compliance, Adjourns Proceedings

Alleged 419 Case: Senator Abdu Kwari in Fresh Court Battle Over Property Deal

Maradin, Dan Saran and Wakilin Watsa Labaran Zazzau Honour Loyal Aides with Traditional Titles