Tinubu ya rantsar da Muttaqha Darma a matsayin ministan gidaje

Tinubu ya rantsar da Muttaqha Darma a matsayin ministan gidaje



Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Dr. Muttaqha Rabe Darma a matsayin Ministan Gidaje da Raya Birane, bayan amincewar majalisar dattawa.

Darma ya maye gurbin Ahmed Musa Dangiwa da ya yi murabus kwanan nan.

A wajen bikin rantsarwar da aka gudanar a fadar gwamnati da ke Abuja, Tinubu ya bayyana cewa nadin ya zo ne a wani muhimmin lokaci na ci gaban ƙasa, yana mai jaddada cewa ana buƙatar ƙwararrun mutane domin tafiyar da harkokin gwamnati.

Sabon ministan ƙwararre ne a fannin gudanarwa da ci gaba, inda ya yi karatu a Jami'ar Bayero Kano da kuma wasu jami’o’i na ƙasashen waje. Ya taɓa riƙe mukamai da dama a jihar Katsina, ciki har da kwamishinan ayyuka da na raya karkara.

Sanarwar rantsarwar ta fito ne daga bakin mai ba shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga.

Comments

Popular posts from this blog

Zazzau Emir’s Defamation Case: Court Bars Claimant Over Non-Compliance, Adjourns Proceedings

Alleged 419 Case: Senator Abdu Kwari in Fresh Court Battle Over Property Deal

Maradin, Dan Saran and Wakilin Watsa Labaran Zazzau Honour Loyal Aides with Traditional Titles