Yusuf Buhari ya baiyana buƙatar da ta tsayawa takarar dan majalisar wakilai
Ɗan marigayi tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, wato Yusuf Buhari, ya baiyana aniyarsa ta tsayawa takara a zaɓen 2027.
Manema labarai sun rawaito cewa Yusuf na son yin takarar kujerar Majalisar Wakilai da yankin Sandamu/Daura/Mai’Adua a jihar Katsina, ƙarƙashin jam’iyyar APC.
Wani tsohon mai taimaka wa shugaban ƙasa kan yaɗa labarai, Bashir Ahmad, ne ya bayyana hakan a shafinsa na X, inda ya ce Yusuf ya ɗauki wannan mataki ne bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki na yankin na su.
Comments
Post a Comment